in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Habasha ya sanar da neman kujerar babban sakataren hukumar WHO
2016-05-25 14:08:11 cri
A jiya Talata ne ministan harkokin wajen kasar Habasha Tewodros Adhanom ya sanar da shiga zaben neman kujerar babban sakataren hukumar kiwon lafiya ta WHO a hukunce.

Mr. Adhanom ya bayyana haka ne a yayin babban taron kiwon lafiya na kasa da kasa karo na 69, a cikin tarihin WHO mai shekaru kusan 70, babu wanda ya taba jagorantar kungiyar daga kasashen Afirka, a halin yanzu, Mr. Adhanom ya samu goyon bayan kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU da wasu kasashen Afirka, a watan Janairu na shekarar bana ne kungiyar AU ta zabi Mr. Adhanom a matsayin dan takara daya tilo daga fadin Afirka da zai shiga zaben neman mukamin babban sakataren hukumar WHO.

A wannan rana, Mr. Adhanom ya bayyana a birnin Geneva cewa, idan ya lashe zaben babban sakataren hukumar WHO, zai mai da hankali kan raya ayyukan kiwon lafiya daga tushe a duk fadin duniya, da kuma kyautata kwarewar hukumar WHO wajen fuskantar ayyukan gaggawa, a sa'i daya kuma, zai dukufa wajen kyautata yanayin kiwon lafiyar mata da kananan yara da dai sauransu.

A matsayinsa na shahararren masani kan cutar zazzabin cizon sauro, Mr. Adhanom ya taba zama ministan harkokin kiwon lafiya a kasar ta Habasha daga shekarar 2005 zuwa shekarar 2012, haka kuma, ya taba zama babban jami'i a Asusun yin rigakafi da ba da agaji kan cutar kanjamau, tarin fuka da kuma zazzabin cizon sauro da wasu kungiyoyin kasa da kasa da abin ya shafa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China