Hukumar Habasha ta sanar da cewa, wasu dauke da makamai na kasar Sudan ta kudu sun kutsa kai cikin kasar Habasha, sun kuma kai hari kan fararen hula na kasar Habasha. Yanzu sojojin kwantar da kura na kasar Habasha suna farautarsu, kuma ya zuwa yanzu an riga an hallaka masu dauke da makamai 60 na kasar Sudan ta kudu.
Sannan hukumar Habasha ta bayyana cewa, ya zuwa yanzu babu abin da ya shaida cewa ko wannan lamari yana da alaka da gwamnati ko masu adawa da gwamnati na kasar Sudan ta kudu. (Sanusi Chen)