in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan, Masar da Habasha sun rattaba hannu akan yarjejeniyar Nile
2015-12-30 10:55:00 cri
Kasashen Sudan, Masar da Habasha a ranar talatan nan suka rattaba hannu a kan yarjejeniyar madatsar ruwa na GERD sakamakon taro na kwanaki 3 da aka yi a Khartoum babban birnin kasar ta Sudan.

An dauki shekara daya ana kokarin cimma matsaya a kan yarjejeniyar ta hanyar tattuanawa tsakanin bangarorin da abin ya shafa.

Sai a watan Maris din wannan shekarar ne dai kasashen 3 suka rattaba hannu kan amincewa da ka'idojin Khartoum wanda ya ba da damar cigaba da tattaunawa akan siyasa da sauran batutuwan har ma da nazarin batutuwan domin kare kason kasashen 3 a kogin Nile.

Ministan harkokin wajen kasar Sudan Ibrahim Ghandour a bayanin da yayi ma manema labarai a ranar talatan nan, ya ce cikin yarjejeniyar kasashen 3 sun cimma matsaya kan sanya wani ofishin kasar Faransa ya kammala nazarain da ake yi kan madatsar ruwan na GERD , gami da gaggauta nazarin, da karfafa amincin su da wadannan ka'idojin da kuma aiwatar da taro a kai a kai tsakanin ma'aikatun ruwa da harkokin waje na kasashen 3.

An fitar da jadawalin da za'a kammala nazarin wannan aikin inji Mr Ghandour, a abin da ya bayyana a matsayin abin tarihi wanda ke jaddada kudirin kasashen 3 na shirin gyara tattaunawa da inganta dabarun hadin gwiwwa a dangantakar dake tsakanin su, da kuma ra'ayin da suke da shi tare.

Shi ma a nashi bangaren ministan harkokin wajen Masar Sameh Shoukry ya bayyana jin dadin shi a kan yarjejeniyar, yana mai cewa ta bayyana aniyar kasashen 3 na shawo kan duk wata shinge.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China