in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Habasha sun yi shawarwarin hadin gwiwar samar da kayayyaki
2016-04-07 13:44:45 cri
Ofishin jakadancin Sin dake kasar Habasha, da ma'aikatar harkokin kudi da hadin gwiwar tattalin arziki ta kasar Habasha, sun gudanar da shawarwarin hadin gwiwar samar da kayayyaki a tsakanin kasashen biyu a karo na farko, yayin zaman da ya gudana a ranar 6 ga watan nan a birnin Addis Ababan kasar Habasha. Manufar taron dai ta hada da kafa dandalin mu'amala a tsakanin gwamnatoci da kamfanonin kasashen biyu.

Ministan harkokin kudi da hadin gwiwar tattalin arziki na kasar Habasha Ahmed Shide Mohammed, ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Habasha na fatan amfani da wannan dama, wajen gano ra'ayoyin kamfanonin kasar Sin, da manufofin da suka shafi hakan, don gudanar da ayyukan hadin gwiwar kasashen biyu yadda ya kamata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China