in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman na kasar Sin ya gana da firaministan kasar Habasha
2016-02-01 10:37:55 cri
Manzon musamman na kasar Sin kuma mataimakin ministan harkokin wajen Sin Zhang Ming ya gana da firaministan kasar Habasha Hailemariam Dessalegn a ranar 28 ga watan Janairu, yayin da ya halarci taron koli karo na 26 na kungiyar AU da ziyarar kasar Habasha.

Zhang Ming ya ce, hadin gwiwar da ke tsakanin kasashen Sin da Habasha ya kasance abun koyi ga hadin gwiwar da ke tsakanin kasashe masu tasowa, kuma abun da ya taka muhimmiyar rawa wajen sa kaimi ga raya hadin gwiwa da ke tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika. A watan Disamba na bara, an yi taron koli na dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afrika wato FOCAC a birnin johannesburg cikin nasara, kuma abun da ya cusa kuzari wajen raya dangantakar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika. Kasar Sin tana fatan yin kokari tare da kasar Habasha, don aiwatar da sakamakon da shugabannin kasashen biyu suka cimma a yayin taron, ta yadda za a karfafa hadin gwiwar moriyar juna daga dukkan fannoni a tsakaninsu, tare da kyautata dangantakar kasashen biyu zuwa wani sabon matsayi, da kawo moriya ga kasashen biyu da jama'arsu.

A nasa bangare kuma, Hailemariam yana mai cewa, kasar Sin abokiya ce kuma babbar kawa ta kasar Habasha, ya kuma jinjina gudummawar da Sin ta bayar wajen raya tattalin arzikin kasar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China