in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ya kalubalanci Sudan ta Kudu da ta yi bincike kan harin da aka kaiwa mafakar ta
2016-02-20 12:23:49 cri
Kwamintin sulhu na MDD ya ba da wata sanarwa a jiya Jumma'a 19 ga wata, inda ya yi Allah wadai da harin da aka kaiwa mafakar da ta kafa a Sudan ta Kudu, kuma ya kalubalanci kasar Sudan ta Kudu da ta yi bincike kan lamarin.

Harin dai ya auku a wata mafakar da majalisar ta kafa a Malakale, wani muhimmin birni dake arewa maso gabashin Sudan ta Kudu, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane a kalla 18, yayin da wasu 50 suka jikkata, hakan ya sa da kakkausar murya, kwamitin ya yi tir da wannan danyen aikin da aka yi.

Kwamitin kuma ya ce, majalisar ta yi Allah wadai da duk wani matakin da fafutuka suka yi wa fararen hula ko MDD. Ban da wannan kuma, ya yi kira ga bangarori daban-daban masu ruwa da tsaki da su yi hakuri don kauracewar haifar da rikici mai tsanani, sai dai kuma ya kalubanci Sudan ta Kudu da ta yi bincike nan da nan kan lamarin karkashin taimakon da tawagar musamman ta MDD dake Sudan ta Kudu ke bayarwa.

Kakakin babban magatakardan MDD Mista Stephane Dujarric ya nuna a ran 19 ga wata cewa, Mista Ban Ki Moon zai kai ziyarar aiki a Sudan ta Kudu a mako mai zuwa don gana da shugaban kasar Mista Salva Kiir Mayardit, tare kuma da kai ziyara a mafakar da majalisar ta kafa a kasar don baiwa 'yan gudun hijira taimako. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China