in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 50,000 na ciki tsananin bukata a sanadiyyar rikicin Sudan ta kudu, inji MDD
2016-02-05 10:23:11 cri
Ofishin kula da aikin jin kai na MDD OCHA ya fada a Alhamis din nan cewar, kungiyoyin bada agaji sun kiyasta cewa mutane dubu 50 ne a yankin Mundri dake jihar yammacin Equtoriya ta kasar Sudan ta kudu suke cikin matsananciyar bukata, a sanadiyyar barkewar tashin hankali a 'yan watannin da suka wuce.

Farhan Haq, shine mataimakin jami'i mai Magana da yawun MDD ya ce sakamakon tabarbarewar tsaro ya hana masu kai agajin samun damar shiga yankunan domin kai kayan tallafi, sai dai suna ci gaba da tuntubar bangarorin da abin ya shafa domin samun damar shigar da kayayyakin agaji yankunan.

Haq, ya ce, a halin yanzu suna rarraba muhimman kayayyakin jinkai na amfanin gida ga mutane kusan 17,500 wadanda ke neman daukin gaggawa a yammacin Mundri, daga cikin su har da wadanda suka yi hasarar kayayyakin su, da wadanda wuta ta kone musu kaya.

Ya kara da cewa, a watan Disambar shekarar 2015, an raba kayayyakin jinkai ga mutane dubu 10 a yankin.

Wani rahoto ya bayyana cewer, Sudan ta kudu na cikin mawuyacin hali, inda aka kiyasta mutane sama da miliyan 7 ne ke fama da karancin abinci, da barazanar barkewar cutar Malariya a jaririyar kasar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China