in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD: dukkanin sassan da rikicin kasar Sudan ta kudu ya shafa sun aikata laifukan keta hakkin bil'adama
2016-01-22 10:44:43 cri
Wani rahoton hadin gwiwa wanda tawagar wanzar da zaman lafiya a Sudan ta Kudu wato UNMISS, da ofishin MDD mai kula da kare hakkin bil'adama suka fitar, ya nuna cewa dukkanin sassa biyu dake fada da juna a rikicin kasar Sundan ta kudu, sun aikata laifuka da dama masu alaka da cin zarafin bil'adama da kuma karya dokokin yaki.

Rahoton wanda MDDr ta fitar a jiya Alhamis, ya zargi tsagin dakarun gwamnatin Sudan na SPLA da na 'yan tawayen SPLM/A-IO da nuna karfin tuwo, a ci gaba da dauki ba dadin da suke yi da juna, tun bayan barkewar tashe-tashen hankula shekaru biyun da suka gabata.

Rahoton ya kara da cewa tashe-tashen hankula sun fi tsananta a yankin daga shekarar 2013 kawo yanzu, musamman ma tsakiya da kuma karshen shekarar. Bincike ya nuna cewa cikin yankuna da dama da fadace-fadacen suka shafa, kalilan ne ke cikin yanani na tsaro a yanzu haka, kasancewar wuraren ibada da asibitoci, da ma sansanonin 'yan gudun hijirar MDD, su ma ba su tsira daga hare-haren mayaka ba.

Cikin wata sanarwa da ya fitar game da wannan batu, kwamishina mai lura da harkokin kare hakkin bil adama na MDD Zeid Ra'ad Al Hussein, ya ce yawaitar cin zarafin mata, da bautar da mutane, tare da kisan gilla da ake yiwa jama'ar yanki, da shigar da dubban yara kanana ayyukan soji, tare kuma da raba al'ummar yankin da matsugunan su, abubuwa ne da ya wajaba a gaggauta dakatar da aukuwar su. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China