in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD tayi tur da barkewar tashin hankali a Sudan ta kudu
2016-02-19 09:47:35 cri
Ofishin shirin tabbatar da zaman lafiya na MDD a Sudan ta kudu UNMISS yayi Allah wadai da barkewar tarzoma a yankin Malakal dake arewa maso magabashin kasar a lokacin da jami'anta ke bakin aiki na kare fafaren hula a kasar.

Mai Magana da yawun MDD Stephane Dujarric, ya shedawa 'yan jaridu cewar matasa 'yan kabilar Shilluk da Dinka ne suka afkawa junansu inda suka yi amfani da wasu kananan makamai da wukake a daren jiya.

A cewar rahoton binciken farko da UNMISS ta gudanar, an hallaka 'yan gudun hijira 5, yayin da aka jikkata mutane 30 a rikicin.

Dujarric ya ce, fadan ya ci gaba da bazuwa har zuwa wayewar gari, sai dai ofishin MDD ya gargadi al'ummomin da su kai zuciya nesa, kuma su warware duk wata takaddama dake tsakanin su ta hanyar tattaunawa.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China