in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sudan ta Kudu ya yi alkawarin girmama yarjejeniyar zaman lafiya
2015-10-25 13:16:39 cri
Shugaban kasar Sudan ta Kudu Salva Kiir, dake ziyarar aiki a kasar Afrika ta Kudu, ya bayyana niyyarsa a ranar Asabar cewa zai dukufa wajen aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya da aka cimma a cikin watan Augustan da ya gabata tare da 'yan tawaye.

Haha kuma, bayan ya gana da takwaransa na kasar Afrika ta Kudu Jacob Zuma a birnin Pretoria, mista Kiir ya yi imanin cewa akwai kalubaloli da dama wajen aiwatar da wannan yarjejeniya, amma ya rantse cewa za'a jure su.

Mista Salva Kiir ya yi wannan ziyara kuma domin karfafa huldar dangantaka a fannonin siyasa da tattalin arziki dake tsakanin kasashe biyu, da kuma neman goyon bayan gwamnatin Afrika ta Kudu wajen daidaita rikicin siyasa a Sudan ta Kudu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China