in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar ma'aikatan jin kai ta samu kaiwa ga wadanda suka rasa muhallan su a Sudan ta kudu
2015-11-10 09:59:31 cri
Sakamakon makonni da aka kwashe ana tabka fada da tarwatsa mazauna, tawagar ma'aikatan jin kai sun samu kaiwa ga mutanen da suka rasa muhallan su kusan 24,000 da suke zaune a yammacin kasar Sudan ta kudu da kayayyakin taimakon kananan yara, ruwan sha da kayayyakin tsabtace jiki, inji kakakin MDD Stephen Dujjaric.

A ganawar sa da manema labarai, kakakin ya ce tawagar ta kuma samu kaiwa ga makwabtan yankuna kamar su Mundri ta gabas da yammacin yankuna duk dai a jihar yammacin Equatorial domin su yi kididdiga da kuma samar da kayyakin kiwon lafiya da sauran abubuwan da ke bukata.

Tawagar sun yi kiyasin cewa kusan mutane 50,000 ne suka rasa matsuguni da kuma suke bukatar taimakon gaggawa na abincin, ruwan sha da matsugunni a yankunan biyu.

Kakakin majlissar ya ce kaiwa ga mutanen da ke da bukatar taimako a yammacin Equatorial ya zama wani babban kalubale saboda mafi yawansu suna boye ne a cikin daji sun kaurace ma kauyukan su.

Tashin hankali ya barke ne da harbe harbe mai tsanani tun kusan farkon watan Augusta tsakanin kabilu masu dauke da makamai a Yambio babban birnin jihar Yammacin Equatorial na kasar. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China