in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi Allah wadai da tashin hankali a Sudan ta kudu
2016-02-19 10:35:55 cri
Sakatare janar na MDD Ban Ki-moon, yayi tur da tashin hankalin daya barke cikin dare a sansanin 'yan gudun hijira na yankin Malakal dake arewa maso gabashin Sudan kudu.

Kalaman na mista Ban sun nuna cewar, duk wani yunkurin tada tarzoma kan fararen hula a harabar da jami'an aikin wanzar da zama lafiya na MDD suke, tamkar aikata laifukan yaki ne.

Mai Magana da yawun Sakatare Janar na MDD Stephane Dujarric, ya fada cewar, Ban ya damu matuka game da zaman tankiya dake wanzuwa tsakanin al'ummar kabilun Dinka da Shilluk.

Ban, ya gargadi alummomin biyu dasu kai zuciya nesa, kuma su guji aikata duk wani abin da ka iya haddasa barkewar tashin hankali a tsakanin su.

Sanarwar ta kara da cewa Ban ya shawarci gwamnati, da jami'an tsaro, da dukkan masu ruwa da tsaki dasu sa ido, domin hana duk wani yunkuri na tada husuma a harabar ofishin MDD.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China