in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 85 sun mutu sakamakon hare hare a Nijeriya
2016-02-02 13:27:05 cri
Shugaban hukumar kiwon lafiya na jihar Borno a Nijeriya Haruna Mshelia, ya shedawa manema labaru a Litinin din nan cewa, an kaddamar da hare hare kan wasu kauyuka uku dake daura da birnin Maiduguri tun daga ranar 30 ga watan Jarairu, hare haren da aka kaddamar a yankin ya yi sanadiyyar mutuwar mutane a kalla 85, yayin da wasu daruruwan suka jikkata.

Wadannan 'yan ta'addanci sun kona gidaje fiye da 300 tare da yin garkuwa da mazauna kauyukan. Rundunar tsaro da masu aikin sakai, sun gano gawawwaki 85 a wuraren da lamarin ya faru, sannan ana ci gaba da kula da wadanda suka samu raunuka a asibiti.

Rahotanni na cewa, sojojin kasar sun yi musayar wuta da mayakan na tsawon sa'o'i 4, yanzu haka hankulla sun fara kwantawa a yankunan da lamarin ya faru. Sai dai har ya zuwa yanzu, babu wata kungiya data yi ikirarin daukar alhakin kaddamar da hare haren. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China