Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya maida martani game da rasuwar Sinawa 3 a kasar Mali sakamakon harin da aka kai, inda ya bayyana takaici da alhini ga iyalan mamatan, tare kuma da ba da umurni ga hukumomin kasar Sin da su dauki matakai da suka dace don ba da tabbaci ga aikin da aka sanya gaba, da kuma kara karfin tsaro ga hukumomi da kamfanonin dake kasashen waje da tabbatar da lafiyar Sinawa dake kasashen ketare. (Amina)