in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin kiyaye zaman lafiya da Sin ta tura zuwa Mali karo na uku sun tashi daga birnin Dalian
2015-05-21 20:54:01 cri
A daren yau Alhamis 21 ga wata, rukuni na farko mai kunshe da hafsoshi da sojoji 190 na rundunar sojan kiyaye zaman lafiya da Sin ta tura zuwa kasar Mali karo na uku ya tashi daga birnin Dalian na Sin cikin jirgin saman haya na MDD, domin maye gurbin sojojin Sin dake gudanar da aikin kiyaye zaman lafiya a yankin Gao a kasar Mali.

Baki daya rundunar sojan kiyaye zaman lafiya da Sin ta tura zuwa Mali karo na uku tana kunshe da membobi 395, wadanda suka hada da injiniyoyi, da jami'an tsaro, da kuma likitoci. Wa'adin aikinsu ya kai tsawon watanni 8. An raba su zuwa rukunoni biyu don zuwa kasar Mali. Manyan ayyukansu sun hada da tabbatar da tsaron ofishin kwamandan dake yankin gabas na tawagar MDD a Mali, da yin gyare gyare ga hanyoyi da gadoji da hanyoyin saukar jiragen sama da dakunan sojoji da sauransu, da ba da jiyya da jigilar sojoji masu kamuwa da cututtuka da sojoji masu jikkata da dai makamantansu.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China