in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala shirya rukunin sojojin Sin na biyu na kiyaye zaman lafiya da za a tura kasar Mali
2014-07-31 15:45:28 cri
An gudanar da taron kaddamar da rukunin sojojin Sin na biyu, na kiyaye zaman lafiya wadda za a tura zuwa kasar Mali, a sansanin sojoji dake birnin Shenyang na nan kasar Sin.

Rukunin dai na kunshe da dakarun soji 395, wadanda suka hada da sojoji ma'aikata, da na masu tabbatar da tsaro da kuma reshen likitoci.

Ofishin kula da harkokin kiyaye zaman lafiya na ma'aikatar tsaron kasar Sin ya bayyana cewa, rukunin sojin na biyu, zai tashi zuwa kasar Mali ne cikin watan Satumba mai zuwa.

Kaza lika ofishin ya ce za a jibge sojojin ne a birnin Gao, inda za su gudanar da ayyukan ginin hanyoyi da gadoji, da gyara hanyoyin filayen jiragen sama, da gine-ginen sansanin soja, da tabbatar da tsaro a sansanin, da kuma aikin jinya ga marasa lafiya da dai sauransu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China