in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana bakin ciki sakamakon rasuwar Sinawa 3 a Mali, in ji Wang Yi
2015-11-21 15:45:25 cri
A yau asabar 21 ga wata a birnin Kuala Lumpur na kasar Malaisiya, a lokacin da yake tsokaci game da rasuwar Sinawa uku lokacin da aka kai hari tare da yin garkuwar da mutanen cikin otel din Radisson Blu na Bamako a kasar Mali, Mr. Wang Yi, ministan harkokin wajen kasar Sin ya bayyana cewa, kasar ta yi alla wadai kan wannan tashin hankali na rashin imani sannan gaba daya shugabannin kasar Sin suna mai da hankulansu kwarai kan lamarin. Haka kuma in ji shi kasar ta nemi ma'aikatar harkokin wajenta da ta shirya tattara duk bayanan da ake bukata yadda ya kamata, har ila yau ofishin jakadancin kasar Sin dake kasar Mali yana iyakacin kokarin daidaita wannan lamarin.

Wang Yi ya kara da cewa, wadannan Sinawa injiniyoyi uku wadanda aka hallaka su sun ziyarci kasar Mali ne domin taimakawa neman ci gaban kasashen Afirka da kawo alheri ga 'yan Afirka. Ana bakin ciki kwarai game da rasuwarsu, sakamakon haka, ya ce gwamnati na mika ta'aziyyarta ga iyalan wadannan mutane.

Har ila yau ya ce kasar Sin na da imani cewa, dukkan jama'ar kasashen Afirka su ma su yi suka da kakkausar murya da kuma kyamar irin wannan mummunan matakin ta'addanci maras tausayi.

Ministan harkokin wajen Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin tana tsayawa tsayin daka kan matsayin yakar ta'addanci da ake yi ta kowace hanya kuma a kowane wuri, sannan tana ganin cewa, ya kamata gamayyar kasa da kasa ta dauki kwararan matakai na yin hadin gwiwa domin yakar ta'addanci yadda ya kamata. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China