in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Mali sun alkawarta zurfafa hadin gwiwa a fannin aikin soji
2015-11-20 09:48:40 cri

Mataimakin shugaban hukumar koli ta ayyukan sojin kasar Sin Fan Changlong, ya ce kasar sa za ta zurfafa hadin gwiwa da kasar Mali a fannin ayyukan soji.

Mr. Fan wanda ya bayyana hakan yayin zantawar sa da ministan tsaron kasar Mali Tieman Coulibaly jiya Alhamis a nan birnin Beijing, ya kara da cewa Sin da Mali kawaye ne na kut da kut, kana Sin na daukar Mali a matsayin aminiya a nahiyar Afirka, wadda kuma ta dade tana hadin gwiwa da Sin a harkokin da suka shafi kasa da kasa.

Ya ce Sin na da burin kara taka rawar da ta dace a bangaren wanzar da zaman lafiya da lumana a Mali.

A nasa bangare Coulibaly, godewa mahukuntan kasar Sin ya yi bisa tallafi da suke baiwa Mali a tsahon lokaci, yana mai fatan bangarorin biyu za su kara azama wajen fadada hadin gwiwarsu a fannin ayyukan soji, ciki hadda ayyukan wanzar da zaman lafiya da kuma horas da jami'ai.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China