in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan tsaron kasar Sin ya gana da takwaransa na Mali
2015-11-16 21:15:25 cri
A yau Litinin 16 ga wata ne ministan tsaron kasar Sin Chang Wanquan, ya yi shawarwari da takwaransa na kasar Mali Tieman Hubert Coulibaly a nan birnin Beijing.

Yayin zantawar tasu, minista Chang ya bayyana cewa, a cikin shekaru 55 da suka gabata, tun bayan kulla huldar diplomasiyya tsakanin Sin da Mali, kasashen biyu sun gudanar da hadin gwiwa a fannoni daban daban. Ya ce Sin na nuna goyon baya ga kasar Mali wajen kiyaye ikon mulkin kan ta, da cikakken yanki da kuma tsaron kasar. Kaza lika Sin za ta yi biyayya ga manufar da shugaba Xi Jinping ya gabatar kan kasashen nahiyar Afirka, sa'an nan za ta hada kan sauran kasashen duniya domin tabbatar da zaman lafiya, da kwanciyar hankali a Mali cikin dogon lokaci.

A nasa bangare, Tieman Hubert Coulibaly godiya ya yi ga kasar Sin game da goyon baya da taimakon da take baiwa kasar Mali cikin dogon lokaci. Ya kuma yi fatan bangarorin biyu za su karfafa hadin gwiwa tsakaninsu a fannonin horar da jami'ai, da kiyaye zaman lafiya a tsakaninsu, tare da sada zumunci tsakanin rundunonin soja na kasashen biyu.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China