in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yi kira da a kara karfin yaki da ta'addanci a nahiyar Afrika
2015-04-11 17:11:30 cri

Kungiyar tarrayar kasashen Afrika AU ta yi kira da a kara karfin yaki da ta'addanci a nahiyar Afrika.

AU ta ba da wata sanarwa a ranar Juma'a cewa, a yayin taronta karo na 497 da aka yi a ranar Alhamis, kwamiti mai kula da zaman lafiya da tsaro (PSC) na kungiyar ya tattauna kan harin da aka kai garin Garissa dake arewa maso gabashin kasar Kenya a ran 2 ga wata.

Ban da wannan kuma, kwamitin ya yi tir da wannan hari, inda kungiyar Al-Shabaab ta kutsa kai cikin jami'ar Moi da ke Garissa tare da kashe dalibai da ma'aikata 148, da kuma jikkata wasu da dama.

Haka zalika, a cewar kwamitin, ganin yadda halin da ake ciki ke kara tsananta dalilin ta'addanci, ya kamata a kara karfin yaki da ta'addanci bisa ka'idar kungiyar AU da kasa da kasa dake da nasaba da wannan lamari. Ban da haka kuma, ya yi kira ga kasashe mambobin kungiyar AU da abokanta da su yi iyakacin kokarin tinkarar ta'addanci, tare kuma kara hadin gwiwa tsakaninsu a wannan fanni.

Dadin dadawa, kwamitin nan na kula da zaman lafiya da tsaro na kungiyar tarayyar Afirka ya sake nanata alkawarin daukar matakan da suka dace, ta yadda kwamitinsa na yaki da ta'addanci zai iya aiwatar da ayyukansa yadda ya kamata. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China