in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yi Allah wadai da harin ta'addanci da aka kai ga kasar Tunisia
2015-03-20 10:36:45 cri
Kungiyar AU ta yi Allah wadai da harin ta'addanci da aka kai ga kasar Tunisia a Laraba 18 ga wata, wanda ya haddasa mutuwar mutane a kalla 21. Kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta yi kira da a hada kai wajen yaki da ta'addanci da masu tsattsauran ra'ayi.

Shugabar kwamitin kungiyar AU Nkosazana Dlamini-Zuma ta nuna rashin jin dadi ga harin ta'addanci da aka kai ga dakin adana kayayyakin tarihi na Bardo dake kasar Tunisia a Laraba, ta bayar da sanarwa cewa, kwamitin kungiyar AU ya yi tir da wannan harin ta'addanci, da jajantawa iyalan mutanen da suka mutu a sakamakon harin, da gwamnati da jama'ar kasar Tunisia.

Kana Madam Zuma ta yi kira ga jama'a da gwamnatin kasar Tunisia da su yi kokarin tabbatar da demokuradiyya da zaman lafiya a kasar.

Ban da wannan kuma, shugabar kwamitin na AU ta jaddada cewa, harin ta'addanci da aka kai ga Tunisia ya nuna cewa, ana bukatar kasashen Afirka da su kara yin hadin gwiwa wajen yaki da ta'addanci da masu tsattsauran ra'ayi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China