in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU: Sin na matukar tallafawa shirin wanzar da zaman lafiya a Afirka
2015-01-31 15:55:21 cri
Wakilin musamman na kungiyar hadin kan Afirka a Somaliya Maman Sidikou, ya ce kasar Sin ta kasance babbar kawa ga nahiyar Afirka, musamman a fannin wanzar da zaman lafiya da lumana.

Sidikou wanda ke jagorantar tawagar wanzar da zaman lafiyar kungiyar ta AU a Somaliya ko AMISOM a takaice, ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labaru da ya gudana a jiya Jumma'a, yayin babban taron AUn karo na 24, dake gudana a birnin Addis Ababan kasar Habasha.

Ya ce goyon bayan da kasar Sin ke baiwa kungiyar AU da tawagar AMISOM a fannin shimfida zaman lafiya, ya nuni ga kasancewarta aminiya ga nahiyar Afirka baki daya.

Kaza lika Sidikou ya jinjinawa kamfanonin kasar Sin bisa sha'awar da suka nuna, na zuba jari a Somaliya, baya ga tallafin da Sin din ke baiwa tawagar AMISOM. Ya ce Sin na daya daga cikin kasashen da suka fara bude ofishinsu a birnin Mogadishu, fadar gwamnatin Somaliya. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China