in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilan kasashen Afirka sun gana gabanin babban taron AU
2015-01-24 17:29:01 cri
Wakilan kasashen Afirka sun gudanar da shawarwari, ciki hadda batun bunkasa harkokin mata, yayin taro na 29, na wakilan dindindin a kwamitin gudanarwar kungiyar AU.

An dai bude zaman ne a jiya Juma'a, a hedkwatar kungiyar AU dake birnin Addis Ababan kasar Habasha, gabanin babban taron AU karo na 24 dake tafe a karshen watan nan na Janairu.

Wakilai daga kasashen nahiyar Afirka sun tattauna game da batun aiwatar da shirin bunkasa harkokin mata, da ake shirin kaddamarwa a wannan shekara, shirin da ke kunshe da manufofin inganta rayuwar 'ya'ya mata daga bana zuwa shekarar 2063.

Cikin jawabin da ya gabatar, mataimakin shugabar kwamitin gudanarwar kungiyar ta AU Erastus Mwencha, ya ce lokaci ya yi, da kasashen Afirka za su hada gwiwa, su fuskanci alkibla daya, domin dora nahiyar kan turbar hadin kai da samun ci gaba, matakin da zai baiwa nahiyar damar samun daukaka mai dorewa cikin yanayin zaman lafiya da lumana.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China