in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugabar kwamitin kungiyar AU ya yabawa kasar Sin game da taimakawa kasashen Afirka wajen yaki da cutar Ebola
2015-01-29 10:45:24 cri
Mataimakin shugabar kwamitin kungiyar AU Erastus Mwencha, ya jinjinawa kasar Sin bisa muhimmiyar rawar da take takawa, a fannin taimakawa kasashen yammacin Afirka wajen yaki da cutar Ebola.

Mwencha wanda ya bayyana hakan a hedkwatar kungiyar ta AU dake birnin Addis Ababan kasar Habasha, ya kara da cewa, baya ga samar da kudi, da magunguna, da na'urori ga kasashe masu fama da cutar Ebola, kasar ta Sin ta kuma aike da likitoci zuwa wadannan kasashen, domin taimakawa wajen yaki da cutar ta Ebola.

Kana Mwencha ya ce, a halin da ake ciki, an samu ci gaba a yakin da ake yi da cutar ta Ebola a kasashen yammacin Afirka, sai dai duk da haka akwai bukatar karin lokaci, kafin a kai ga shawo kan cutar baki daya a wannan karo.

Haka zalika, Mwencha ya ce yayin taron koli na kungiyar AU karo na 24, wanda za a gudanar a ranar 30 zuwa 31 ga wannan wata, za a tattauna game da kafa cibiyar rigakafi, da yaki da cututtuka ta Afirka, a wani mataki na tabbatar da hana yaduwar cutar ta Ebola. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China