in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin waje na kasar Sin ya gana da shugaban kwamitin wasannin Olympic
2015-03-31 10:18:15 cri

Ministan harkokin waje na kasar Sin Wang Yi wanda ya halarci taron ministocin harkokin waje masu tattauna batun nukiliyar kasar Iran da aka yi a birnin Lausanne dake kasar Switzerland ya gana da shugaban kwamitin wasannin Olympic Thomas Bach a dakin ajiye kayayyakin tarihi na wasannin Olympic a yammacin ranar Litinin.

Yayin ganawar, Mr. Wang ya ce, tun hayewa kujerarsa, Mr. Bach ya yi iyakacin kokarin gudanar da ayyukan kirkire-kirkire don sa kaimi ga wasannin motsa jiki na Olympic.

Ban da wannan kuma, Mr. Wang ya ce, birnin Beijing da na Zhangjiakou na Sin na kokarin neman daukar nauyin shirya wasannin Olympic na yanayin hunturu na shekarar 2022, da zummar sa kaimi ga miliyoyin Sinawa da su shiga ayyukan motsa jiki, matakin da zai yada tunanin Olympic da wasannin motsa jiki irin wanda aka yi a kan dusar kankara. Sin a nata bangare na da karfi kuma ta cancanta ta dauki nauyin shirya wannan gasa.

A nashi bangare, Mr. Bach ya ce, kwamitinsa na darajanta tunanin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya dauka na baiwa jama'ar kasar kwarin gwiwar yin motsa jiki. Kwamitin kuma ya hada kai da Sin cikin dogon lokaci, yana fatan za a inganta hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu nan gaba. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China