in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya yi maraba da bakin kasashen waje masu halartar bikin rufe gasar wasannin Olympics ta matasa a birnin Nanjing
2014-08-29 10:23:15 cri

Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya shirya liyafa a birnin Nanjing a ranar Alhamis 28 ga wata don yin maraba da manyan baki masu halartar bikin rufe gasar wasannin Olympics ta matasa karo na biyu, da suka hada da shugaban kwamitin wasannin Olympics na duniya Thomas Bach, shugaban kwamitin wasannin Olympics na duniya da aka girmamawa Jacques Rogge, firaministan kasar Madagascar Kolo Roger, firaministan kasar Antigua da Barbuda da sauransu.

A cikin jawabinsa, Li Keqiang ya nuna godiya ga kwamitin wasannin Olympics na duniya a madadin gwamnatin kasar Sin bisa ga goyon baya da gudummawar data baiwa gasar wasannin Olympics ta matasa a birnin Nanjing, sannan kuma ya taya 'yan wasa daga kasa da kasa murnar samun kyakkyawan sakamakon gasanni.

Haka nan kuma Li Keqiang ya yi nuni da cewa, gudanar da gasar wasannin Olympics ta matasa a birnin Nanjing cikin nasara zai kara inganta mu'amala da hadin gwiwa a tsakanin matasan kasar Sin da na kasashen duniya, da kara fahimtar juna da sada zumunta a tsakanin jama'ar kasar ta kasa da kasa, da kuma sa kaimi ga samar da zaman lafiya mai dorewa da wadata a duniya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China