in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Faransa ta yaba wa kokarin Nijar wajen yaki da Boko Haram
2015-02-23 17:23:01 cri
Ministan harkokin wajen kasar Faransa Laurent Fabius, wanda ya isa birnin Niamey a ranar Lahadi a yayin wani rangadin aiki na yaki da ta'addanci, ya bayyana cewa yana nuna yabo sosai kan matakin da Nijar ta dauka wajen yaki da kungiyar Boko Haram.

Kafin ya sauka babban birnin Nijar, minista Laurent Fabius sai da ya yada zango ranar Asabar a birnin N'Djamena na kasar Chadi da kuma birnin Yaounde na kasar Kamaru, a wani rangadin da ya shafi taka birki ga kungiyar Boko Haram musammun ma a wadannan kasashe uku dake makwabtaka da Najeriya.

Mista Fabius ya samu ganawa tare da shugaban kasar Nijar Mahamadou Issoufou jim kadan bayan saukarsa ranar Lahadi a fadar shugaban kasar dake birnin Niamey.

A yayin taron manema labarai na hadin gwiwa tare da takwaransa na kasar Nijar Bazoum Mohamed, mista Laurent Fabius ya bayyana cewa sakamakon annobar Boko Haram, ya sa kasashen Nijar, Chadi da Kamaru, suka dauki mataki dake nuna himma da kwazo wajen yaki da Boko Haram kuma ya kamata gamayyar kasa da kasa ta nuna yabo kansa.

Ya ce ya zo ne domin kawo taimako da goyon bayan kasar Faransa game da wannan muhimmin mataki da kasar Nijar ta dauka. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China