in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijar ta kuduri anniyar yaki da ta'addanci, bayan mutuwar sojojinta 9 a kasar Mali
2014-10-04 20:58:19 cri
Kwana daya bayan mutuwar sojojin wamzar da zaman lafiya na MDD 'yan asalin Nijar a kasar Mali a yayin wani harin ta'addanci a arewacin kasar Mali, shugaban Nijar Mahamadou Issoufou ya bayyana a ranar Asabar cewa wannan ba zai karya lagon Nijar ba wajen cigaba da yaki da ta'addanci.

Za mu cigaba da tsayawa kasar Mali domin dafawa wannan manufa mai kyau, domin yakin da muke yi, yaki mai daraja, dalilin muna kishin demokaradiya ne, za mu iyakacin kokarin mu domin kawo na mu taimako wajen kawar da ta'addanci a yankin Sahara in ji shugaban kasar Nijar.

Jami'an tsaron mu zasu cigaba da kawo nasu taimako a cikin tawagar MINUSMA, a kasar Mali ko a wani wuri, idan aiki ya kira mu to za mu je in ji Mahamadou Issoufou.

Sojojin Nijar 9 dake cikin rukunin Nijar da aka tura Mali na tawagar wanzar da zaman lafiya a kasar Mali (MINUSMA) aka kashe a ranar Jumma'a a wani kwantan bauna na wasu mayakan ta'addanci da ba'a tantance su ba, a tazarar kilomita 80 daga garin Menaka dake yankin Gao a yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa Ansongo a kuriyar arewacin Mali domin daukar kayayyaki.

Tun cikin watan Agusta, aka tura wani rukunin sojan Nijar na biyu dake kunshe da mutane 850 a arewacin Mali.

Nijar da Mali na raba kan iyakar kasa guda bisa tsawon kilomita fiye da 800, kana al'ummomin wurin na amfani da harsuna iri daya wato Tamajek, Songhoi, fulfulde da sauransu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China