in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ba a kammala yarjejeniyar hadin gwiwwa da wani kamfanin Faransa na hakar ma'adinai ba, in ji jami'in Nijar
2014-07-22 20:52:34 cri
Kakakin majalissar dokokin kasar Nijar Hama Amadou ya sanar da cewa yarjejeniyar da aka rattaba ma hannu a ranar 26 ga watan Mayu tsakanin gwamnatin kasar da wata kamfanin hakar ma'adinai ta kasar Faransa Areva ba a kammala shi ba.

A cikin yarjejeniyar,an amince cewa rassan kamfanonin biyu za su nada 'yan kasar ta Nijar a matsayin Darektoci tsakanin watan Yuni na 2014 zuwa 2016.

Malam Hama Amadou yayi bayanin cewa yanzu haka an dakatar da hakar sinadarin na uranium wanda zai sa kasar ta zama ta biyu a duniya wajen hako wa inda zata samar da tan 5000 duk shekara na sinadarin har sai an samu daidaituwa a kasuwannin duniya.

A dangane da hakan kakakin majalaissar ya zargi kamfanin da daukan matsayin da zai amfana mata ita kadai yana mai cewa dakatar da hakan sinadarin a yanzu haka zai kawo matsalar rashin aikin yi ga matasan kasar da dama.

Ita dai wannan kamfanin hakar ma'adinan ta kasance wadda take hakar sinadarin Uranium a yankin agadez dake arewacin kasar ta hannun rassan ta guda biyu wato Somair da Cominak fiye da shekaru 50 da suka gabata.

(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China