in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Nijar zai halarci bukukuwan tunawa da zuwan sojojin kawance a kudancin Faransa karo a karo 70
2014-08-15 16:00:30 cri
Shugaban kasar Nijar Mahamadou Issoufou zai halarci bukukuwa karo na 70 na tunawa da zuwa sojojin kawance a kudancin Faransa a ranar Jumma'a a birnin Toulon na kasar Faransa, a cewar wata majiya mai tushe a ranar Alhamis.

Shugaban kasar Faransa Francois Hollande zai jagoranci bukukuwan a karo na 70 na zuwa sojojin kawance a kudancin Faransa tare da shugabanni kusan ashirin da gwamnatocin kasashen Afrika dake kudu da hamadar Sahara.

Zuwan sojojin kawance a wannan yanki ya kasance wani aikin soja da aka gudanar a lokacin yakin duniya na biyu daga shekarar 1939 zuwa shekarar 1944) inda daga ranar 15 ga watan Augustan shekarar 1944 sojojin Faransa, Ingila, Amurka da Afrika suka isa kudancin Faransa domin kwato kasar daga hannun sojojin kasar Jamus, lamarin da ya kawo karshen yakin. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China