in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijar da Faransa sun rattaba hannu kan yarjejeniyoyin shiga na kusan Sefa biliyan 49
2014-07-19 16:23:22 cri
Kasashen Nijar da Faransa ta hanyar asusun cigaba na kasar Faransa (CFD) sun rattaba hannu a ranar Jumma'a a Niamey kan wasu yarjejeniyoyi shida a fannoni daban daban a yayin ziyarar shugaban kasar Faransa Francois Hollande a wannan kasa.

Yarjejeniyoyi na jimillar kudin Euro fiye da milyan 74, kwatankwacin kudin Sefa biliyan 49, sun shafi fannoni daban daban wadanda suka hada kiwon lafiyar yara, kanana 'yan kasa da shakaru biyar na haihuwa, makamashi tare da fafada layin wutar lantarki na kamfanin wutar lantarki na kasa NIGELEC, fannin ilimi, noma da kiyo a yankuna goma sha daya da aikin gina madatsar ruwa Kandaji ya shafa, da kuma tsaron abinci. Baya ga wannan kuma akwai taimakon kungiyar tarayyar Turai na kusan Sefa biliyan 8.

Francois Hollande ya isa Niamey a ranar Jumma, bayan ya fito daga birnin Abidjan na kasar Cote d'Ivoire tare da wata babbar tawagar dake kunshe da manyan 'yan kasuwa. A Niamey, wadannan manyan 'yan kasuwa na Faransa sun yi tattaunawa tare da takwaransu na kasar Nijar. Shugaban kasar Faransa ya bar Niamey a ranar Jumma'a da yamma zuwa birnin N'djamena na kasar Chadi a matsayin zangon karshe na wannan rangadi nasa a Afrika. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China