in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kayayyakin agaji da Sin ta samar ga Senegal sun isa Dakar
2014-11-01 20:42:45 cri
Da sanyin safiyar ranar 1 ga watan Nuwambar nan ne jirgin saman dake dauke da kayayyakin agaji da gwamnatin kasar Sin ta samar ga kasar Senegal domin hana yaduwar cutar Ebola ya isa filin sauka da tashin jiragen saman kasa da kasa dake babban birnin kasar, Dakar.

Wannan dai shi ne karo na uku da kasar Sin ta aike da kayayyakin agaji zuwa Afirka. Wadannan kayayyaki dai sun hada da tufafin kariya, da na'urar auna zafin jiki da dai sauransu.

Jakadan kasar Sin dake kasar Senegal Xia Huang ya bayyana cewa, hakan na cikin muhimman matakai da kasar Sin ke dauka wajen taimaka wa kasashen dake fama da cutar, kuma tallafin zai ba da taimako matuka ga gwamnatin kasar ta Senegal game da hana yaduwar cutar Ebola a kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China