in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kafofin watsa labaran kasa da kasa sun nuna yabo kan kudurin da kasar Sin ta dauka na neman bunkasuwa bisa doka
2014-10-25 16:53:24 cri
An zartas da wani kuduri dangane da wasu muhimman batutuwa kan yadda za a kara inganta hanyoyin tafiyar da harkokin mulkin kasa bisa doka daga dukkan fannoni a yayin cikakken zaman 4 na kwamitin tsakiya na Jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin karo na 18 da aka kammala a ran 23 ga wata, don gane haka, wasu kafofin watsa labaran kasa da kasa suna ganin cewa, kudurin ya nuna babban burin kasar Sin wajen tafiyar da harkokin mulkin kasa bisa doka sosai, ya kuma bayyana kudurin kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar kan inganta wannan aiki.

Bisa labarin da jaridar New York Times ta kasar Amurka ta bayar a kan yanar gizonta, an ce, wannan ne karon farko da cikakken zaman kwamitin tsakiya na Jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya mai da tafiyar da harkokin mulkin kasa bisa doka a matsayin babban taken taron, kwaskwarimar da aka yi game da dokokin kasa za su kyautata tsari da yanayin adalci na dokokin kasar Sin yadda ya kamata.

Haka zalika, jaridar Les Echos ta kasar Faransa ta ba da labarin cewa, a yayin taron, an tattauna kan yadda za a iya tafiyar da harkokin mulkin kasa bisa doka, inda aka kuma fitar da matakai da dama dangane da aikin, lamarin ya nuna aniyar jam'iyyar kwaminis ta Sin sosai kan yin kwaskwarima a kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China