in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen duniya sun yaba wa kudurin da kwamitin tsakiya na JKS ya zartas don gane da zurfafa yin gyare-gyare
2013-11-16 17:23:02 cri
Bayyanar kudurin da kwamitin tsakiya na JKS ya zartas kan wasu manyan batutuwa da suka shafi zurfafa yin gyare-gyare a dukkan fannoni, ta sanya kasashen duniya mai da hankula sosai kan wannan batu.

Kafofin watsa labaru na kasa da kasa da dama sun yi sharhi kan wannan batu, tare da bayyana gamsuwa ga kudurin da kwamitin na tsakiya na JKS ya gabatar, suna masu cewa, kuduri ne da ba a taba ganin irinsa a tarihi ba.

Har ila yau kafofin sun bayyana hanyar gurguzu da Sin ke bi, da cewa, hanya ce da ta dace a yi maraba da ita. Wannan takarda dai ta nuna cewa, matakan yin gyare-gyare da Sin za ta yi, ba a taba ganin irinsu a tarihi ba, za kuma su zama wata taswirar zurfafa yin gyare-gyare a dukkan fannoni.

Ra'ayin kasashen duniya kan wannan kuduri ya shafi bangarori masu yawan gaske, ciki hadda ra'ayin kamfanonin watsa labaru na AP da Reuters, da sauran manyan kafofin yada labaru. Kamfanin Reuters ya ce, wannan takarda ta shafi ayyukan yin gyare-gyare a fannoni da yawa. A sa'i daya kuma, jama'a daga sauran kasashe ciki har da Rasha, da Faransa, da Ingila, da New Zealand da dai sauransu sun tattauna kan kudurin da kwamitin tsakiya na JKS ya zartas.(Danladi)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China