in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Faransa sun sha alwashin kara hadin kai wajen yaki da Ebola
2014-10-19 20:12:34 cri
Kasashen Sin da Faransa suna mai da hankali sosai kan annobar cutar Ebola da ke addabar yammacin Afrika, ministan harkokin waje na kasar Sin Wang Yi da takwaransa na kasar ta Faransa Laurent Fabius sun yi musanyar ra'ayi kan wannan batu a yau Lahadi 19 ga wata a nan birnin Beijing, inda bangarorin biyu suka yi alkawarin kara hadin gwiwa domin yaki da cutar.

Bangarorin biyu sun nuna gamsuwa sosai kan mu'ammalar da ake yi tsakanin wasu hukumomin nazarin cututtuka nasu, musamman ma cibiyar yin rigakafi da shawo kan cututtuka ta kasar Sin da cibiyar nazari ta Pasteur ta Faransa, da kwalejin nazarin lafiyar jiki na Faransa da asusun Merieux, ban da haka kuma, suna farin ciki sosai domin ganin yarjejeniyar hadin gwiwa da cibiyar sa ido kan lafiyar jiki ta Faransa da cibiyar yin rigakafi da shawo kan cututtuka ta kasar Sin za su daddale, inda bangarorin biyu sun yi alkawarin cewa, za su hada kai wajen yin nazari da shawo kan kwayoyin cuta ta yin amfani da dakin nazari na P4 dake birnin Lyon na Faransa da dakin nazari na P4 da ake kokarin kafawa a birnin Wuhan na kasar Sin, har ma da kara hadin gwiwa a wurare da ke fama da cutar ta Ebola ta fuskar aikin jin kai da yin musanyar fasahohi tsakanin rukunnonin ba da jiyya, ban da haka kuma, kasashen biyu za su yi kokarin hadin kai da wasu kasashe dake yammacin Afrika da cutar ta fi kamari, domin baiwa musu taimakon inganta tsarin kiwon lafiya. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China