in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ganawa tsakanin shugabannin Sin da Maldives
2014-09-15 20:44:08 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar ta Maldives a yau Litinin 15 ga wata a birnin Male. Inda bangarorin biyu suka yi musayar ra'ayi kan wasu batutuwan dake jawo hankalinsu, kana sun cimma matsaya daya wajen kafa dangantakar abokantaka ta sada zumunci a dukkan fannoni.

Kazalika, bayan ganawar, shugabannin biyu sun halarci bikin sa hannu kan yarjejeniyoyin hadin kai da suka shafi fannonin diplomasiyya, cinikayya, muhimman ababen more rayuwa da sauransu.

Ban da haka kuma, shugabannin biyu sun zanta da manema labaru, inda shugaba Xi ya jaddada cewa, kasashen biyu sun yanke shawarar kafa sabuwar dangantakar hadin kai a dukkan fannoni, abin da ya samar da makoma mai haske a hadin gwiwar da ke tsakaninsu tare da kara bunkasa dangantakar dake tsakaninsu. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China