in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kafofin watsa labaru sun mai da hankali kan ziyarar shugaban kasar Sin a kasar Mongolia
2014-08-23 15:49:50 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai ziyara a kasar Mongolia daga ranar 21 zuwa ta 22 ga watan nan na Agusta. A yayin ziyararsa, bangarorin Sin da Mongolia sun kulla yarjeniyoyin da suka shafi harkar diplomasiyya, tattalin arziki, ciniki, aikin sufuri, hada-hadar kudi, al'adu, albarkatun kasa da dai sauransu. A sa'i daya kuma, kafofin watsa labarai na kasashe daban daban sun mai da hankali sosai kan wannan ziyara ta shugaba Xi, da kuma yadda kasashen Sin da Mongolia suka kulla huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare.

Kamar yadda kamfanin dillancin labarun kasar Mongolia ya rawaito a ranar 22 ga wata cewa, shugaban majalisar dokokin kasar, Zandankhuu Enkhbold ya nuna godiya kan yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai ziyara a kasarsa, tare da kulla yarjeniyoyi masu muhimmanci tare da bangaren Mongolia, inda ya ce takardun da aka sa hannu a kai za su taka muhimmiyar rawa wajen karfafa hadin kai da mu'ammala tsakanin kasashen 2.

A nasa bangaren, rediyon Muryar Rasha ya ba da labari a ranar 22 ga wata cewa, ziyarar da shugaba Xi ya kai a Mongolia ita ce karon farko da wani shugaban kasar Sin da ya kai a kasar cikin shekaru 11 da suka gabata. Haka zalika, shugabannin kasashen 2 sun yi amfani da wannan dama domin tattaunawa kan wasu manyan batutuwa, ta yadda za su iya gudanar da hakikanin hadin gwiwa. Wannan ziyara, a cewar Muryar Rasha, ta sheda cewa kasashen Sin da Mongolia suna kokarin kyautata huldar dake tsakaninsu da neman hadin kai a wasu sabbin fannoni. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China