in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya yi jawabi a majalisar dokokin kasar Mongolia
2014-08-22 16:50:10 cri
Yau Jumma'a 22 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ba da wani muhimmin jawabi a majalisar dokokin kasar Mongolia, mai taken "hadin kai wajen kafa sabuwar dangantaka tsakanin kasar Sin da kasar Mongolia", inda Mr. Xi ya nuna kyakkyawar fata kan hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu, inda ya bayyana manufofin diflomasiyyar kasar Sin da zama tare a tsakanin kasashen Asiya.

Bugu da kari, shugaba Xi ya jaddada muhimmancin girmama juna, fahimtar juna, taimakawa juna da kuma cin moriyar juna, don bunkasa sabuwar dangantakar abokantaka tsakanin kasar Sin da kasar Mongolia, ta yadda za a iya ciyar da bunkasuwar yankin Asiya gaba daya.

A jawabinsa, Mr. Xi ya jaddada cewa, ya kamata kasar Sin da kasar Mongolia su tsaya tsayin daka wajen taimakawa juna yadda ya kamata, duk da canje-canjen da ake fuskanta a harkokin kasa da kasa, sannan ya kamata kasashen biyu su kiyaye dangantakar dake tsakaninsu bisa fahimtar juna, da kuma tsayawa tsayin daka kan nuna goyon baya ga juna wajen kiyaye ikon mulkin kasa, tsaro da cikakken yankin kasa.

Bugu da kari, shugaba Xi ya bayyana cewa, a halin yanzu, yankin Asiya shi ne yankin mafi saurin bunkasuwar tattalin arziki, a sa'i daya kuma, yankin Asiya na fuskantar matsaloli da dama da abin ya shafa, don haka ya kamata kasashen dake yankin Asiya su inganta dangantakar dake tsakaninsu yadda ya kamata don samun ci gaba tare, wanda ya zama wani babban aiki ga dukkanin kasashen dake yankin na Asiya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China