in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwayoyin cutar Ebola ba su shiga kudancin nahiyar Afirka ba
2014-08-14 20:14:26 cri
Kwanan baya, hukumar kiwon lafiya ta kasa da kasa ta WHO ta sanya kasar Kenya dake gabashin nahiyar Afirka cikin jerin kasashen da mai iyuwa za su yi fama da yaduwar cutar Ebola, lamarin da ya cusa damuwa matuka ga sauran kasashen da cutar ba ta shiga ba a halin yanzu, sabo da mai iyuwa ne, cutar Ebola za ta yadu daga yammacin kasashen nahiyar Afirka zuwa sauran kasashen. Kana, a halin yanzu, ba a samu bullar cutar a kudancin kasashen Afirka ba, amma dangane yadda jama'a ke kai koma tsakanin kasashen, ya sa kasashen da abin ya shafa suke ci gaba da karfafa matakan kandagarki, da na jan hankulan al'umma, kana lamarin bai kawo illa ga yanayin karko na zamantakewar al'umma ba.

Haka kuma, gamayyar kungiyar bunkasa kudancin kasashen Afirka ta SADC ta kira wani taron musamman na ministocin kiwon lafiyar mambobin kasashen gamayyar, don tattaunawa kan yadda za a iya fuskantar lamarin, idan cutar Ebola ta yadu zuwa kudancin kasashen na Afirka. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China