in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nigeriya ta samu mutuwar wanda ya kamu da Ebola karo na hudu.
2014-08-15 10:23:52 cri
Nigeriya a ranar Alhamis din nan ta samu rahoton mutuwar wata mai aikin jinya sakamakon cutar Ebola, abin da ya kai adadin wadanda suka rasu a wannan hali zuwa hudu.

Ita dai wannan mata ta bada jinya ne ga Patrick Sawyer dan asalin kasar Liberiyan nan da ya fara zuwa da cutar a jihar Ikko, ya kuma mutu a ranar 25 ga watan jiya, kamar yadda kafofin yada labaran kasar suka sanar.

Matar ta rasu ne da safiyar Alhamis din nan a babban asibitin gwamnati na Yaba dake Ikko, duk da cewa har yanzu ba'a fitar da wata sanarwa a hukumance ba tukuna.

Kafin haka wata mai aikin jinya da ita ma ta kula da lafiyar Sawyer kafin mutuwarsa ta rasu a makon da ya gabata, sannan wani ma'aikaci a ofishin kungiyar tarayyar tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS dake Ikkon shi ma ya rasu ranar Talatan nan da ta shige.

Gwamnatin Nigeriya dai a ranar Litinin ta riga tabbatar da cewa yanzu haka akwai rahoton mutane 10 da suka kamu da cutar ban da wadansu 177 da ake sa musu ido a gani ko akwai alamu a tare da su.

Jumma'an da ta gabata, shugaba Goodluck Jonathan ya sanar da dokar ta baci a kan cutar, inda ya ce za'a fitar da kudi Naira biliyan 1.9 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 11.6 domin gudanar da ayyukan ba da kariya da hana yaduwar cutar. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China