in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO ta jaddada cewa ba za a bada umurnin hana yin yawon shakatawa a kasashe masu fama da cutar Ebola ba
2014-08-15 14:28:54 cri
Hukumar kiwon lafiya ta duniya wato WHO ta jaddada a ranar 14 ga wata cewa, akwai wuya ne da yada cutar Ebola a yayin da ake tafiya ta jiragen sama, don haka babu bukatar da a ba da umurnin hana yin yawon shakatawa a kasashe masu fama da cutar Ebola.

Shugabar sashen yin kashedi da tinkarar halin dokar ta baci ta WHO Isabelle Nuttal ta bayyana a gun taron manema labaru cewa, cutar Ebola ta sha bamban da cutar mura da tarin fuka, ba ta yaduwa ta iska, sai dai ana kamuwa ta hanyar yin mu'amala kai tsaye kawai. Kana cutar tana iyar yaduwa bayan da alamun kamuwa da cutar suka bullo. Don haka, idan wani mutum dake da alamun kamuwa da cutar yana cikin jirgin sama a sararin samaniya, hadarin kalilan ne na yiwuwar sauran fasinjoji da ma'aikatan jirgin su taba ruwan jikin wannan mutum kai tsaye.

Bisa sabuwar kididdigar da hukumar WHO ta yi, an ce, ya zuwa ranar 11 ga wata, mutane 1975 na kasashen Guinea, Liberia, Saliyo da Nijeriya sun tabbatar da kamuwa da cutar, ko aka zarge su da kamuwa da cutar, kuma 1069 daga cikinsu sun rasa rayukansu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China