in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ba ta amince da ziyarar mambobin majalisar ministocin Japan a haikalin Yasukumi ba
2014-08-15 16:15:01 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Madam Hua Chunying a zantawarta da manema labaru a Jumma'an nan 15 ga wata a nan birnin Beijing, ta ce, Sin ta sake kalubalantar Japan da ta daidaita matsaloli dake da nasaba da ziyarar da mambobin majalisar ministocin Japan suka yiwa haikalin Yasukumi.

An ba da labarin cewa, wasu mambobin majalisar ministocin Japan a yau Jumma'a 15 ga wata sun kai ziyara a haikalin Yasukumi, sannan kuma firaminista Shinzo Abe ya mika kudin yin ibada.

A cewar Madam Hua, haikalin Yasukumi ya mara baya ga wadanda suka aikata laifin yaki cikin babban yakin duniya na biyu, tare da yin alfahari da laifufukan da suka yi, yadda shugaban kasar ya mikawa haikalin kudin yin ibada wani abu ne da ya bayyana matsayi na kuskure da gwamnatin Japan ke dauka kan tarihi. Hakan ya sa, Sin ta nuna matukar rashin jin dadi.

Bugu da kari, Madam Hua ta yi nuni da cewa, dangantakar dake tsakanin Sin da Japan na iya samun ci gaba muddin kasar ta daidaita matsayin da ta dauka kan harin da ta kai da yin watsi da ra'ayin karfin soja. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China