in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ba za ta yarda a tada zaune tsaye a wasu yankuna ba tare da yin la'akari da tsaron wasu kasashe ba
2013-12-09 20:31:02 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin waje na kasar Sin Mr Hong Lei ya bayyana a ranar Litinin din nan 9 ga wata a nan birnin Beijing cewa, Sin ba za ta yarda da ko wace kasa da ta tada zaune tsaye a wasu yankuna ba tare da yin la'akari da tsaron wasu kasashe ba.

An ba da labari cewa, ministan tsaron kasar Japan Onodera Itsunori ya gana da takwaransa na kasar Philiphines Voltaire Gazmin a ranar Asabar din da ta gabata 7 ga wata, inda bangarorin biyu ke ganin cewa, matakin da Sin ta dauka na kafa yankin shata sassan tsaron sararin samaniyar tekun Kudu zai haifar da rikici a yankin Asiya-Pacific. Inda a nasa bangare Onodera Itsunori ya yi kira ga kasashen duniya da su nuna rashin jin dadi kan lamarin.

Da yake maida martani game da wannan bukata Mr Hong a gun taron manema labarai Litinin din nan 9 ga wata ya ce, Sin na nan a kan matsayinta na tsaron kasar, don haka ko kusa ba za ta yarda a tsoma mata baki kan harkokin cikin gidanta ba. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China