in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi maraba da ci gaba da tsagaita bude wuta da Palesdinu da Isra'ila suka yi
2014-08-14 20:17:31 cri

An labarta cewa, a daren ranar 13 ga wata, kasashen Palesdinu da Isra'ila sun amince da tsawaita wa'adin tsagaita bude wuta a zirin Gaza zuwa kwanaki 5, wanda zai cika nan ba da dadewa ba, don haka bangarorin 2 za su ci gaba da shawarwarin da suke kan tsagaita bude wuta cikin dogon lokaci a birnin Alhakira, hedkwatar kasar Masar.

Dangane da hakan, Madam Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta ce, yanzu haka Palesdinu da Isra'ila suna shawarwari a Alkahira. Kasar Sin ta yi kira da su kai zuciya nesa a yayin da suke tsagaita bude wuta, su gaggauta yin shawarwarin yadda ya kamata, a kokarin cimma wata yarjejeniyar tsagaita bude wuta na dogon lokaci. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China