in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan ci gaba da shiga tsakani kan batun nukiliyar kasar Iran
2014-06-09 20:44:02 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Madam Hua Chunying ta shedawa manema labarai a yau Litinin 9 ga wata a nan birnin Beijing cewa, Sin na fatan hada kai da bangarori daban-daban da batun nukiliyar kasar Iran ya shafa domin shiga a dama da ita kan wannan batu tare da ba da gudunmawarta.

An ba da labari cewa, ma'aikatar harkokin wajen kasar Iran ta sanar a ran 7 ga wata cewa, Iran za ta yi shawarwari kai tsaye da Amurka da Rasha kan batun nukiliyarta, sannan, za ta tattauna da sauran bangarorin da batun ya shafa gaba da gaba

Game da wannan batu, Madam Hua ta bayyana wa manema labaru a wannan rana cewa, tun farkon wannan shekara da muke ciki, kasashe shida da wannan batu ya shafa sun riga sun sulhunta a dukkan fannoni da Iran sau hudu, yanzu za a yi sabon zagaye na tattunawa daga ran 16 zuwa 20 ga wannan watan. Yayin da ake fuskantar tafiyar hawainiya wajen yin shawarwarin, abubuwa dake gaban bangarorin daban-daban za su kara wuya, abin da ya sa ake bukatar bangarorin daban-daban da su kawar da bambancin ra'ayi dake tsakaninsui. A ganin Sin, yadda kasashen 6 suke kokarin musayar ra'ayi da bangaren Iran zai taimakawa samun fahimtar juna tsakaninsu, da ciyar da aikin shawarwarin gaba.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China