in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya kara wa'adin aikin kungiyar ba da taimako ga Somalia da ofishin kiyaye zama lafiyar Guinea Bissau
2014-05-30 16:04:35 cri
Jiya Alhamis 29 ga wata, kwamitin sulhu na MDD ya zartas da kudurori biyu, inda ya kara wa'adin aikin kungiyar ba da taimako ga Somalia ta MDD da ofishin kiyaye zama lafiya na MDD dake Guinea Bissau.

Bisa kudurin farko, kwamitin ya kara wa'adin aikin kungiyar ba da taimako dake Somalia zuwa watanni 12, domin ta ci gaba da gudanar da aikin shiga tsakani a kasar, da goyon bayan yunkurin gwamnatin kasar na shimfida zaman lafiya da zaman jituwa a kasar, da ba da shawarwari kan yadda za a iyar tabbatar da zaman lafiya da bunkasuwar kasar, da ba da taimako wajen kyautata ayyukan gwamantin kasar, gami da bincike da ba da rahoto kan yanayin hakkin dan Adam na kasar.

Sa'an nan game da kuduri na biyu, kwamitin ya kara wa'adin aikin ofishin kiyaye zaman lafiyar dake Guinea Bissau zuwa watanni 6. Haka kwamitin ya yi maraba da nasarorin da kasar Guinea Bissau ta samu wajen gudanar da babban zabe da zaben majalisar dokokin kasar, inda yana ganin cewa, ya kamata ofishin ya ba da taimako wajen farfadowar wannan kasa a fannoni daban daban, kiyaye tsarin mulkin kasar, da kara azama ga yin shawarwari a duk fadin kasar bayan zaben. Bugu da kari, an kuma jaddada cewa, ya kamata a kira wani taron kasa da kasa kan ba da taimakon kudi don tallafa wa kasar Guinea Bissau samun farfadowa cikin sauri. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China