in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara kada kuri'u a babban zaben kasar Guinea Bissau
2014-04-13 20:33:01 cri
Dubban al'ummar kasar Guinea Bissau ne suka fara kada kuri'un su a Lahadin nan, a babban zaben kasar na farko tun bayan juyin mulkin sojin shekarar 2012. Juyin mulkin da ya kai ga hambarar da tsohon shugaban kasar Raimundo Pereira, ya kuma jefa kasar cikin mawuyacin hali.

Ana dai sa ran 'yan kasar su kimanin 775,000 ne zasu kada kuri'un su, yayin zaben na shugaban kasar, da 'yan majalissun dokoki.

Akwai dai 'yan takara 13 dake neman kujerar shugabancin kasar, yayin da kuma jam'iyyu 15 suka fidda 'yan takarar neman kujerun majalisun dokoki.

Cikin manyan 'yan takarar kujerar jagorancin kasar akwai tsohon ministan kudin kasar Jose Mario Vaz na jam'iyyar PAIGC, da Abel Lamedi Incada, da kuma Paulo Gomes. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China