in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani babban jami'in tsaron Saliyo ya ce, ba za su janye dakarunsu daga Somaliya ba duk da barazanar da suke fuskanta
2013-10-01 16:46:21 cri
Ministan tsaron kasar Saliyo Alfred Paolo Conteh ya fada a ranar Litinin 30 ga watan Satumba cewa, kasar ta Saliyo ba za ta janye dakarunta daga kasar Somaliya ba, duk da barazanar da kungiyar Al-Shabaab ke yi.

Ministan ya ce, Saliyo ta kasance wani bangare na kasashen da ke bayar da gudummawar dakaru, kamar yadda yarjejeniyar kungiyar AU ta tanada, inda ya ce, wannan shi ne abin da kasar za ta saka wa Afirka da shi kan irin taimakon da ta baiwa Saliyo a lokacin yakin basarar da aka shafe shekaru goma ana yi a kasar, wanda aka kawo karshensa a shekarar 2002.

Conteh ya ce, abin da ya shafi daya daga cikin kasashen Afirka, hakika ya shafi sauran kasashen na Afirka, don haka ya ce, "idan har muka nade hannu muna kallon abin da ke faruwa a kasar Somaliya, to, tasirin hakan na iya shafar mu."

Ita dai kungiyar Al-Shabaab, reshen kungiyar Al-Qaeda ne da ke da mazauni a Somaliya, kuma Saliyo ta tura kimanin sojoji 800 da 'yan sanda 55 zuwa Somaliya, sannan nan ba da dadewa ba wani rukuni mai kunshe da 'yan sanda 150 zai tashi zuwa kasar ta Somaliya. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China