in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta bada agajin hatsi ga Guinea Bissau don maganci karanci abinci da take fama da shi
2013-08-06 20:35:17 cri
Kasar Sin za ta bada agajin hatsi ga kasar Guinea Bissau domin ta magance karancin abincin da take fuskanta kamar yadda sabon jakadan Sin a kasar Wang Hua ya bayyana yau Talata 6 ga wata.

Mr. Wang wanda ya bayyana hakan bayan rattaba hannu da ya yi akan wata yarjejeniyar aiwatar da wannan aiki tare da firaministan Kasar Rui Duarte Barros, ya ce wannan agajin yana cikin taimakon da Sin ta yi niyyar baiwa kasar sakamakon bukatar hakan da ta nuna, dangane da yunwar dake barazanar kamar al'ummarta saboda karancin abinci, musammam ma a kauyukan karkara.

Sai dai jakadan bai bayyana adadi ko kwatancin nawa ne agaijn zai kama ba.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China