Firaministan kasar Austriliya Tony Abbott ya tabbatar a birnin Shanghai na kasar Sin cewa, "Yanzu mun san inda akwatin nadar bayanan jirgin sama na Malaysia yake, kuma za a kokarin gudanar da binciken gano wannan na'ura cikin wani yankin ruwan teku mai fadin muraba'in kilomita daya. Amma nasarar sanin inda wannan na'urar take ba ya nufin cewa, za mu iya gano tarkacen wannan jirgin na Malaysia, amma duk da haka kasar Austriliya za ta ci gaba da hadin kai da Sin da dai sauran kasashe domin lalube shi." (Amina)